Thursday, January 10, 2019

Faruwar Wasannin Kwaikwayo Na Rediyo A Nijeriya


Rediyo kamar yadda sunansa ya ke a Turanci, wata hanya ce ta isar da sa}o ga jama’a na kusa da kuma na nesa, ta hanyar jin sauti ba tare da ganin mai isar da sa}on ba. Rediyo yana ]aya daga cikin hanyoyin mafi sau}i da kuma sauri da ]an Adam ya tanadar wa kansa don biyan bu}atar isar da sa}onni da ilimantarwa da fa]akarwa da kuma nisha]antarwa. Wa]annan abubuwa guda uku su ne babban ma}asudin kafa gidan rediyo ga jama’a a duniya. Gidan rediyo yana ]aya daga cikin kafafen watsa labarai da ]an Adam ya }ir}iro don taimakawa kansa wajen sadarwa.
Shekaru da dama da suka wuce ]an Adam yana da hanyoyin sadarwa daban-daban na gargajiya kamar ihu da kuka da yekuwa da buga wani abu ko ki]a ko kuma busa }aho.
An samu ci gaba a inda ]an Adam ya iya rubutu da karatu daga nan sai ya fara amfani da rubutun yana aikawa da sa}o ta hanyar wasi}a a rubuce, ta haka har aka samu wasi}a mai suna kar-ta-kwana.
Ana kyautata zaton cewa wani Bature mai suna Macconi wanda yake injiniya ne, shi ne ya fara }ir}iro wayar iska tare da yin gwajinta a cikin shekarar 1899, a New York ta }asar Amurka. Wannan }ir}ira ita ta haifar da rediyo ko kuma ilmin }ir}irar rediyo da ake amfani da shi a yau.
A don haka wannan ci gaba na zamani da ]an Adam ya samu ta rayuwa, shi ya bayyana samar da rediyo a ko’ina, a ciki har da Nijeriya. Gidan rediyo na farko da aka fara bu]ewa a Nijeriya shi ne Nigerian Broadcasting Services (NBS) a shekarar 1962, a garin Legas. Wannan gidan Rediyo (NBS) daga baya an canza masa suna zuwa Nigerian Broadcasting Cooperation (NBC), daidai wannan lokacin Nijeriya tana da yankuna guda uku, don haka sai aka yi tashoshi na rediyo a wa]annan ~angarori guda uku, jihar Gabas, da Yamma da Arewa. Wannan shi ne ya haifar da a ranar sha biyar ga watan Maris 1962, aka bu]e Gidan  Rediyon Tarayya na Kaduna. Alh. Sir, Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato, kuma Firimiyan Jihar Arewa, ya bayyana muhimman abubuwa guda uku ake bu}ata a gidan rediyon ya yi wa mutane Arewa. Ga abin da Firimiya ya ce a wajen bu]e wannan gidan Rediyo. Wannan gidan rediyon kamar sauran gidajen rediyo, ana sa ran ya ilmantar, ya nisha]antar ya kuma sanar game da nisha]antarwa kuma akan ce, ta~a ki]a ta~a karatu”.
Bayan an }ir}iro da wannan gidan rediyo na farko a Arewacin Nijeriya aka sa mashi suna Broadcasting Cooperation of Northern Nigeria, watau Hukumar Watsa Labarai ta Jihar Arewa, sai aka du}ufa wajen wayar wa da al’umma Arewa kai ta hanyar ilmantarwa da nisha]antarwa, sannan kuma da sanar da su game da manufofin gwamnatin jihar Arewa. To a lokacin da aka }addamar da wannan Gidan rediyo mai ]auke da ‘yan kayan aiki }alilan, sai masana suka gano cewa wasan kwaikwayo shi ne wata babbar hanyar da za a bi wajen ilmantar da al’umma.
Har ila yau, a shekarar 1976 gwamnatin soja ta Tarayya ta rushe kamfanin NBC ta sake kafa Federal Redio Corporation of Nigeria (FRCN) aka kuma raba yankin Ibadan da Ikko da kuma yankin Kaduna.

Gidan Rediyon Nijeriya na Kaduna shi ne kusan jagoran sauran gidajen rediyo domin kuwa duk sauran gidajen rediyon Nijeriya ta Arewa musamman }asashen Hausa a }ar}ashin yankin Rediyo Kaduna suke. An tabbatar da cewa ta hanyar amfani da rediyo ne za a iya sanar da al’umma abin da gwamnati take ciki tare da ilmantarwa da nisha]antarwa. To ta yin la’akari da haka ya sa wasan kwaikwayo ya zama wata muhimmiyar hanya mafi sau}i wajen isar da sa}o ga al’umma.
Wannan dalili ya sa ake ganin cewa an da]e ana yin wasan kwaikwayo a gidajen rediyon }asar nan. Ana iya cewa wasan kwaikwayo na rediyo an fara shi tun wajen shekarar 1954, amma a nan arewancin Nijeriya ana ganin cewa wasannin kwaikwayo na farko da aka fara gabatarwa a rediyo, an fara su ne a rediyon Tarayya na Kaduna a cikin shekarar 1963. Shirin Noma yanke Talauci, shi ne shiri na farko da aka soma gwadawa cikin shirin wasan kwaikwayo. Dalilin kiran shi wasan kwaikwayo shi ne saboda ana gabatar da shi ne ta yin amfani da yanayin wasa da raha da masu gabatarwar suka yi domin jan hankalin manoma don koyar da su dabarun noma irin na zamani.
Daga wannan shiri kuma sai wasan kwaikwayon “Zaman Duniya Iyawa Ne”. Shi wannan shiri, wani madubi ne na rayuwa, kuma don kada a bar masu saurare da wasan kwaikwayo guda ]aya wanda ya shafi aikin gona kawai sai wani shirin ya fito wanda Alhaji Yusuf Ladan ya rubuta na tsawon shekaru. Wannan shirin yana }unshe da ban dariya da nisha]antarwa.
Daga nan kuma sai aka samu wasan kwaikwayo “Taba sa Farin Cikin Aljihu. Kamfanin Taba Sigari sun sadu da Hukumar Gidan Rediyon Tarayya Kaduna suka bu}aci marubucin wasan Zaman Duniya Iyawa ne ya rubuta wannan wasa na ‘Taba sa Farin Cikin Aljihu’. Wannan shirin ya yi matu}ar kar~uwa don kuwa an sami manoma da dama da suka rungumi noman Taba a wancan lokacin.
Da tafiya-ta-yi-tafiya kuma sai aka fito da wani shiri mai suna “Basafce [an Mallam Dogara na Kumatu Mai Karen Kamun Kura”. Shi wannan wasa ne da ya ke koyar da aikin gona da kiwon lafiya don zama cikin }oshin lafiya. Bayan wannan kuma sai shirin “Gundumi Fasa Kwanya” wasa ne wanda Alhaji Yusuf Ladan ya shirya. Wasan ya shafi dambe na gargajiya. Haka kuma wasa ne wanda ya zama tamkar zakaran gwajin dafi. Wannan wasa ya yi matu}ar amsuwa ga al’ummar Arewacin Nijeriya kuma ya }ara fito da wannan Gidan Rediyo Tarayya na Kaduna.
Daga nan kuma a cikin shekarar 1972 sai wasu shirye-shirye su ka samu wa]anda suka }ara wa harkar wasan kwaikwayo ha~aka a wannan gidan rediyo Nigeria na Kaduna. Wa]annan shirye-shiryen sun ha]a da; shirin Duniya Budurwar Wawa, da Samanja Mazan Fama, wa]anda Usman Baba Pategi yake shiryawa.
Hakan ya taimaka wajen samuwar wasannin kwaikwayo a gidajen Rediyo na jihohin Arewacin }asar nan, misali idan muka dubi gidan Rediyon Kano wato gidan Rediyon da yake bi wa na Kaduna wajen iya gabatar da shirye-shirye, sun yi }o}ari fiye da yadda ake tsammani ta fuskar shirya wasannin kwaikwayo. Wasu daga cikin ire-iren wasannin kwaikwayo da aka gudanar a wannan lokacin sun ha]a da. In Ba Ku Ba Gida; wanda Mrs. Afinike Hamman wata mutuniyar Bauchi ta ke shiryawa tare da taimakon Hassana Umaru da Kulu Suleiman, kuma akwai wasanni kamarsu; Komai da Ruwanka” wanda Mallam Sharif Lawal Adamu ya shirya, sai kuma wasan “Duniyar Nan Tamu” na Malam Abdullahi Sani Makarantar Lungu, Haka kuma akwai wasan “Hannu [aya” wanda shi gidan Rediyo ya ke shiryawa, akwai kuma wasan “Jami’ar Fanisau” wanda yana }unshe ne da raha kuma sukan shirya shi ne domin yin shagu~e ga Gwamnati. Sauran wasanni da aka gabatar a wannan gidan rediyo sun ha]a da; Jatau Na Albarkawa; da Jatau na {yallu, da sauransu.
Haka kuma Gidan Rediyon Jihar Bauchi ya gudanar da wasu wasannin kwaikwayo da suka ha]a da; “Duniya Ina Za Ki Da Mu” wanda Abubakar Aliyu Dori yake shiryawa, da kuma wasan “Yaro Sabon Mutum, wanda Hauwa Muhammad Bin take shiryawa.
          Da haka dai wasannin kwaikwayo su ka yi ta ci gaba da ya]uwa da ha~aka a gidajen Rediyo daban-daban na jiholin Arewacin Nijeriya, kuma kodayaushe ana samun sababbi idan bu}atar yin hakan ta samu. Ko a halin yanzu ana gudanar da wasannin kwaikwayo a gidajen  Rediyo da dama wa]anda suke a jihohin Arewacin }asar nan ciki har da Gidan Rediyon Jihar Kebbi wanda ake gudanar da wannan bincike a kan sa. Wasannin sun kasance wata hanya ko wata kafa ta nisha]antarwa da fa]akarwa tare da ilmantarwa ga dukkanin al’ummomin da ke zaune a wa]annan jihohin.






[1] Tattaunawar da aka yi da wasu ma’aikatan Gidan Rediyon Jihar Kebbi ranar 10/11/2018 a gidan Rediyo.

No comments:

Post a Comment

GASKIYA INA LAIFINKI? Daga Aliyu Muhammadu Bunza

1. Shukuran ga Allah wahidun mai agaji, Da salati gun Manzo aminin shiriya. 2. Na yo yabo matuqa dukan asahabihi, Manyan gwaraje m...